
Lafiya Jari ce
Shirin Lafiya Jari ce na tattaunawa da likitoci da mahukunta a game da kiyon lafiyar jama'a, sanin sabbin magunguna da binciken kimiya ya samar. Ana gabatar da shirin a ranar Littinin da hantsi, tare da maimaici a ranar Jumma'a da safe.
Episodes
Ƙaruwar masu fama da cutar sikila a Jamhuriyar Kamaru
A wannan makon shirin ya yi duba ne kan ƙaruwar masu fama da cutar sikila a jamhuriyyar Kamaru bayan fitar wani rahoto da ke cewa cikin shekara 1 kaɗai an tattara alƙaluman sabbin mutum dubu 6 da aka gano suna ɗauke da cutar. Wannan cuta mai alaƙa da nau’in jini, na daga cikin matakan yaƙi da ita shi ne tabbatar da gwaje-gwajen jini tun kafin aure don kaucewa haifar yara masu ɗauke da ita, ganin c
Illolin da ke tattare da sauya launin fata da wasu mata ke yi
Shirin lafiya Jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda mata suka rungumi tsarin gyaran jiki ta fannoni daban-daban kama daga magungunan sha ko mayukan shafawa ko kuma salon amfani da na’ura da nufin ƙawata sura. Wasu daga cikin batutuwa mafi jan hankali a wannan babi na gyaran jiki shi ne tayar da komaɗar fata da sauran sassan jiki don killacewa ko kuma kange kai daga bayyanar tsufa, k
Illolin magungunan matsi ga lafiyar mata
Shirin a wannan mako zai ɗora ne akan wanda ya gabace shi a makon jiya, sai dai a wannan karon zamu karkata ga illolin da magungunan matsi ke haifarwa ga lafiyar mata, duk da ya ke matan kan yi don bajinta ko nuna isa a wajen mazajensu. Danna alamar sauti don sauraron karin bayani.....
Abubuwan da ke haddasa cutuka ga al'aura ko matantaka ga mata
Shirin Lafiya Jari ce na wannan makon ya yi nazari kan ƙaruwar matan da ke fama da cutuka masu alaƙa da al’aura ko kuma matantaka, tare da laluben hanyoyin magancesu ta hanyar tattaunawa da ƙwararru a wannan fanni, cutukan da ƙwararrun ke alaƙantawa da rashin baiwa al’aurar kariya wanda a lokuta da dama ke haddasa gagarumar matsala. Ku lasha alamar sauti don sauraron shirin tare da Azima Bashir Am
Abubuwan da ya kamata a sani kan sabuwar cutar Hantavirus da ta ɓulla
Shirin Lafiya Jari Ce a wannan makon ya yi nazari kan cutar Hantavirus da duniya ta ga ɓullarta a baya-bayan nan, lamarin da ya sanya fargaba a zuƙatan jama’a, musamman ganin yadda ake alaƙanta wannan cuta a sahun masu haɗari da tarihi ya nuna yaddda suka yiwa duniya ɓarna matuƙa. Cikin watan jiya ne aka ga ɓullar wannan cuta a wani jirgi da ya taso daga Argentina zuwa Cape Verde, sai dai tilas ya
Yadda ake gudanar da yaƙi da cutar polio tsakanin Nijar da maƙwaftanta
Shirin lafiya jari Ce a wannan makon zai nazarci yadda ake gudanar aikin yaki da cutar polio tsakanin ƙasashen makwabtan juna wato Najeriya da Nijar a wani yunƙuri na kakkaɓe ɓurɓushin wannan cuta musamman a yankunan kan iyaka na ƙasashen biyu duk kuwa da saɓanin diflomasiyyar da ke tsakanin gwamnatocin ƙasashen biyu.
Wani bincike ya gano yadda kashi 13 na al'ummar Ghana ke rayuwa cutar ƙoda
A wannan makon shirin na Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu ya yi nazari kan wani bincike can a Ghana da ke ƙiyasta cewa kusan kashi 13.3 na yawan jama’ar ƙasar na rayuwa da cutukan ƙoda, galibi ba tare da masaniyar suna ɗauke da ita ba, lura da yadda cutar bata nuna alamu a farko har sai ta kai ga ta’azzara. Wannan na nuna yadda cutar ta ƙoda ke matsayin babban ƙalubale a Ghana. Binciken m
Yadda tsananin zafin bana ke barazana ga lafiyar jama’a a Arewa
A wannan makon, shirin na Lafiya Jari ce ya mayar da hankali kan tsananin zafin da ake fuskanta a wasu jihohi na yankin Arewacin Najeriya, wanda masana suka yi ittifaƙin ya kai matakin da ka iya haddasa wasu cutuka ko kuma tayar da kwantattu. Zafin na bana ya sha bamban da wanda aka saba gani a kowace shekara, domin jama’a na bayyana cewa ya daɗe bai lafa ba kamar yadda aka saba gani a shekarun ba
An samu raguwar haihuwa a Najeriya sakamakon rungumar tsarin tazarar Iyali
Shirin Lafi Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba ne kan wani rahoton sashen bincike da kula da lafiyar jama’a na NDHS da ke ƙarƙashin hukumar kula da yawan jama’a ta Najeriya NPC, wanda ke nuna cewa daga shekarar 2024 yawan haihuwa ya ragu matuƙa tsakan matan Najeriya daga kashi 5.3 zuwa kashi 4.8. Wannan sakamakon rahoto na NDHS a cewar masana manuniya ce kan yadda mata a
Yadda Cutar Sankarau ke barazana ga wasu ƙasashen yammacin Afirka
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba ne kan cutar ɗan sanƙarau ko kuma meningitis, cutar da a yanzu haka wasu ƙasashe ke cikin haɗarin fuskantar ɓullarta musamman a yammacin Afrika, waɗanda dama ke a tubalin fuskantar wannan cuta lokaci zuwa lokaci.
Kalubalen da ake fuskanta wajan yaki da cutar babban tari ko tuberculosis
Shirin Lafiya Jarice na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali gameda tarin matsaloli da gangamin yaki da babban tari ke cin karo dasu. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin........
Najeriya ta karɓi sabbin alluran rigakafin cutar HIV
Shirin Lafiya Jari ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan sabbin alluran rigakafin cutar Sida ko kuma HIV Aids da Najeriya ta karɓa ƙarƙashin shirin yaƙi da wannan cuta mai haɗari. Danna alamar sauti don sauraron cikakken shiri....
Haɗarin cizon mahaukacin kare da ke haddasa cutar zangai maras jin magani
A wannan makon shirin na lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba kan matsalar cutar zangai ko cizon mahaukacin kare, cutar dake daɗa bazuwa a jamhuriyyar Nijar musaman a Jihar Maradi, jihar dake sahun gaba wajan masu fama da wannan matsala. Alƙaluman ofishin ministan lafiya na jamhuriyyar Nijar sun nuna cewa cikin mutane 10 da cutar ta kashe, 5 sun fito ne daga jihar Maraɗi, inda aka
Jita-jitar dake alaƙanta kamuwa da cututtuka ta hanyar amfani da kayayyakin lantarki
A wannan makon shirin na Lafiya Jari ce ya mayar da hankali kan jita-jitar da ke alaƙanta amfani da wasu kayakin lantarki a matsayin dalilan da ke sabbaba kamuwa da wasu nau’ikan cutuka ciki har da Cancer.A wannan makon shirin na Lafiya Jari ce ya mayar da hankali kan jita-jitar da ke alaƙanta amfani da wasu kayakin lantarki a matsayin dalilan da ke sabbaba kamuwa da wasu nau’ikan cutuka ciki ha
Cututtukan da ke barazana ga lafiyar jama'a a lokacin azumi
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon ya mayar da hankali ne kan irin cututtuka da ke barazana ga lafiyar al'umma a lokacin azumin watan Ramadan, musamman ga masu azumi da ke fuskantar sauye-sauyen lafiyar jiki. Galibi a duk lokacin da aka faro azumi, mutane da dama musamman masu kwantattun cutuka kan taso musamman idan mutane basu ɗauka matakan da suka kamata ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron
Zubar hazo a lokacin zafi ya haddasawa mutane da dama rashin lafiya a Kamaru
A wannan makon shirin na Lafiya Jari ce ya mayar da hankali kan sauyawar yanayin da wani yanki na arewacin ƙasar Kamaru ya gamu da shi a watan Fabarairun da ya gabata wanda ba safai aka saba ganin faruwarsa ba, ta yadda ake ganin zubar hazo a wani yanayi da kuma ake fama da tsananin zafi, wanda ya haddasa cutuka, lamarin da ya sanya gamayyar masana lafiya dana yanayi jan hankali jama’a don su ɗauk
Yadda yakamata jama'a su kula da cimakarsu a lokacin azumin Ramadan
Shirin Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan mako zai mayar da hankali kan cimaka a lokacin azumin watan Ramadana, dama yadda wasu ke fuskantar matsaloli masu alaƙa ɓacin ciki sakamakon yanayin ciye-ciyen da akan yi ko dai a lokacin buɗa baki ko kuma sahur. Kamar yadda ya ke bisa al’ada a irin wannan lokaci na azumin watan Ramadan, musulmi kan ƙauracewa abinci da abin sha tun gabanin
Najeriya ta ƙaddamar da dokar ta ɓaci a harkar kiwon lafiya
A wannan makon shirin zai yi dubi ne kan dokar ta baci a harkan lafiya da gwamnatin Najeriya ta kaddamar inda ta sanar da karuwar cutuka masu alaka da gurbatacciyar iskar da jama’ar ƙasar ke shaka. Hukumar duba gari ta Najeriya ko kuma Environmental Health Council a Turance ita ta sanar da wannan dokar ta baci inda tace munin cutukan dake alaka da numfashi da kuma cutar kansa dake karuwa yasa dole
An fara gangamin rigakafin cutar Typhoid irinsa na farko a Jamhuriyyar Nijar
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan gangamin rigakafin cutar Typhoid da mahukuntan Jamhuriyyar Nijar suka faro a faɗin ƙasar, irinsa na farko da aka taɓa gani a tarihi a wani yanayi da ake ganin ta’azzarar wannan cuta a ƙasar ta yankin Sahel. Wasu alƙaluman hukumar Lafiyar Jamhuriyyar Nijar a 2021 sun ce mutane dubu 30 suka kamu da cutar, a wancan lokaci wadda ta haddasa m
Illolin da sauyin yanayi ke haifarwa ga lafiyar jama'a
A wannan makon shirin Lafiya Jari ce ya mayar da hankali ne kan illolin da sauyawar yanayi ke haifarwa ga lafiyar jama’a, musamman ganin yadda hunturu ya fara amma kuma kwatsam ya ɗauke cikin ƙanƙanin lokaci tare da shigowar zahi, lamarin da ya haddasa cutuka masu yawa a tsakanin jama’a.
Ɓullar annobar ƙyanda ta t'azzara a sassan Najeriya
A wannan makon shirin tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan fitar wasu sabbin alƙaluman hukumar NCDC masu tayar da hankali matuƙa da ke nuna yawaitar ɓullar cutar ƙyanda ko kuma baƙon dauro dama ƙaruwar mutanen da take kashewa a sassan Najeriya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.......
Illar ta'ammali da magungunan ƙara kuzari ko rage gajiya da jama'a ke yi
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan karon ya mayar da hankali kan yadda ɗabi’ar ta’ammali da wasu nau’ikan tsumin gargajiya da sunan samun kuzari ko kuma ƙarfin jiki ke ci gaba da ta'azzara tsakanin jama'a, wanda masana suka yi ittifaƙin na da matuƙar illa ga lafiyar jama’a. Tsumi na baya-bayan nan da ke samun karɓuwa tsakanin jama’a musamman masu ayyukan ƙarfi shi ne ‘’Wanki
Dabarun yaƙi da ƙibar da ta wuce ƙima ko kuma Obesity tsakanin matasa
Shirin Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir a wannan mako ya mayar da hankali kan wasu alƙaluman mujallar Lancet da ke nuna cewa nan da shekarar 2050 fiye da kashi 50 na yawan al’ummar Afrika musamman Afrika za su zama masu ƙibar da ta wuce ƙima ko kuma Obesity a turance. Alƙaluman na Lancet wanda aka tattara bayan gwaji a ƙasashe fiye da 50 ya nuna cewa matsloli masu alaƙa da cimaka da kuma rashin
Bincike ya gano cewa kashi 38 na matan Damagaram ne kaɗai ke haihuwa a asibiti
Shirin Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan makon ya mayar da hankali game da yadda wasu mata a Jamhuriyyar Nijar ke ƙin amincewa da haihuwa a asibiti duk kuwa da haɗarin da ke tattare da haihuwa a gida. Wasu alƙaluman baya-bayan nan da mahukuntan jihar Damagaram suka tattara, ya nuna cewa ƙasa da kashi 40 na mata ne ke haihuwa a asibiti duk kuwa da yadda mahukunta suka mayar da haih











